Ibrahim Shekarau
Ibrahim Shekarau | |||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|
11 ga Yuni, 2019 - 11 ga Yuni, 2023 ← Rabiu Kwankwaso District: Kano Central
Mayu 2003 - Mayu 2011 ← Rabiu Kwankwaso - Rabiu Kwankwaso → District: Kano Central
| |||||||
Rayuwa | |||||||
Haihuwa | Kano, 5 Nuwamba, 1955 (68 shekaru) | ||||||
ƙasa | Najeriya | ||||||
Harshen uwa | Kanuri | ||||||
Ƴan uwa | |||||||
Abokiyar zama | Amina ibrahim shekarau | ||||||
Karatu | |||||||
Makaranta |
Jami'ar Ahmadu Bello Jami'ar Bayero | ||||||
Harsuna |
Turanci Hausa Kanuri | ||||||
Sana'a | |||||||
Sana'a | ɗan siyasa, anti-vaccine activist (en) da administrator (en) | ||||||
Imani | |||||||
Addini | Musulunci | ||||||
Jam'iyar siyasa | New Nigeria Peoples Party (en) |
Malam Ibrahim Shekarau tsohon Malami ne kuma ɗan siyasan Najeriya ne, an haife shi a shekara ta 1955 a Kano, Arewacin Najeriya (a jahar Kano). Ya rike Ministan ilimin Najeriya daga shekara ta 2014 zuwa shekarar 2015. Ya fara takarar Gwamnan jahar Kano a shekara ta 2003, wanda daga bisani ya zamto ya lashe zaben da aka yi a watan Janairun shekara ta 2003, ya yi mulkin jahar har sau biyu sanadiyyar sake samun nasarar da yayi a zaben shekarar 2011, haka ne ya sa ya jagoranci mulkin jahar na tsawon shekaru 8, kafin nan Rabi'u Kwankwaso wanda yayi gwamna kafinsa ya sake dawowa shi ma a karo na biyu inda ya yi takarar matsayin gwamnan jahar a karo na biyu, kwankwason ya yi nasarar lashe Zaben shi ma inda ya yi mulkin jahar a karo na biyu daga watan Mayun shekara ta 2011 zuwa shekarar 2015.
Zargin cin kudin makamai
A halin yanzu Ibrahim Shekarau ya na fuskantar shari'a a gaban kotu bisa zargin haɗa baki da karkatar da kuɗi kimanin miliyan ɗari tara da hamsin wanda wani ɓangare ne daga kudaden da gwamnati ta ware a shekarar 2014 don yaki da masu tada kayar baya amma aka karkatar da su a wancan lokacin don yakin neman zaben shugaba Goodluck Jonathan wanda ofishin mai bada shawara akan harkokin tsaro wanda Sambo Dasuki ya fitar. amma sai dai har yanzu ba a kama shi da laifin ba